AURE RIBAR MASOYA
🥰 ƘASIDA GAME DA AURE 🥰
[ Amshi ]
Ƙarshen maganar so dai ayo aure ribar masoya
Daɗi na zumar so sai cikin aure in har tsakani akwai ƙauna
(1)
Allah Mabuwayi Mai yawan kyauta Mai bada baiwa
Sunanka nasa farko Ka lamince kar in gazawa
Don banida mai tama ni in miƙe ba karkacewa
Sai Kai Ma'ishin Sarki ina fatan yaa Rabbi Ka amsa roƙo na
(2)
Bana iya gegewa a waƙe sai nayo salati
Ga Muhammadu Manzo Annabin tsira Abba ga Fati
Na sanya sahabbai har iyalai tsarkaka a baiti
Na sa mabiya dominko bana tsame wanda ke binsa Manzo na
(3)
Mun wayi gari ranar biki ƙanne harma da yayye
Dangi duka sunzo ga sahun ƴaƴa sannan iyaye
Taro na abokai ɓangaren mata suko ƙawaye
Kowa fara'a an ɗaura auren soyayya a yau mu muna murna
(4)
Allah a cikin tsarinsa dama yace ya ƙawata
Wa maza sha'awar ƙauna da soyayya tsantsa ga mata
Sannan ya nufa aure ya zamto hanyar daƙile ta
Hanya ɗaya tilo wacce kowa ke fatan a sunansa an zana
(5)
Aure ya zamo ƙauna da soyayya sune silarsa
Sannan ya zamo an sanya addini ne ginshiqinsa
Sannan kuma ga tsantsar fahimtar juna ƙarƙashinsa
Nan za kaga daddaɗan zama mai riba babu zance na ban kwana
(6)
Allahu Gwani ya ƙirƙiro mata domin maza ne
Domin natsuwar ɗa sai ta hanyar mataye mu gane
A tsakani soyayya da jin tausai su garkuwa ne
Lallai fa akwai aya cikin wannan tsari idan munbi mun auna
(7)
Aure ni'ima sannan ga bayin Allah garkuwa ne
Hanyar da katangaggu suke zaɓa domin riƙo ne
Don yaɗa tsatson kirki cikin ɗinbin taron mutane
Domin su zamo ƴaƴan da Manzo zai sanya a taron da zai nuna
(8)
Zan ɗanyi nasihata ga angwaye sannan amare
Kuyi mai yiwuwa domin rufe sirrin juna a tare
Haƙuri da kawaici ya zamo tilas ba ware-ware
In kun riƙe wannan kunbi tsarin cin ribar zama ba gudun juna
(9)
Aure fa ibadah ne idan mun gane babu wasa
Sai mun riƙe linzami da kyau don samun dawwamarsa
Mu sani kuma Allah zai yi sakayya ƙarshe akansa
Da wuta yakayi koko idan munyo me kyau ya saka da aljannah
(10)
In har kayi aure to kasan girma yazo gareka
Kiwo na amaryar taka ya komo yau ƙarƙashinka
Ran gobe ƙiyama kansa Allah sai ya tambayeka
Yaya ka gudanar kayi adalci ko ka zamo shugaban ɓarna
(11)
Aure fa idan kayoshi shikenan ka ɗaure kanka
Kai keda salo tsari da hanyoyin samar da doka
A gidanka idan ka kasa yin wannan ka ɓata harka
In har matsala tazo kasan dai kaine zuciya zata sha ƙuna
(12)
Mata ki sani kema tulin haƙƙoƙi ne a kanki
Aiki na miji shine fa jagora kullum na aiki
Saidai fa ibadah wacce ta zarce komai a ɗaki
In kin riƙe wannan Jalla zai kawo ɗaukin da ke zaki amfana
(13)
Ke karɓi batu na shi gidan aure ai dausayi ne
Ki riƙe da kula ɗakin miji taskar ɗibar rabo ne
In kinyi sake zakiy asara mai girma ki gane
Duk wanda ya yayo shuka na sharri ƙarshe dole zai girbi mummuna
(14)
Zan kulle batu ba don gazawa koko gundura ba
Sai don na taƙaice zantuka ba sai na ɗawwala ba
Ba zan hana ɗimbin masu bi jin daɗin ƙafiya ba
Saidai fa ina son fayyace daɗin aure ga duk wanda ke bi na
(15)
Mai bi da kula nine Sulaiman Abban Mustaphan nan
Ɗa gun Uthman ango ga Maryam ƴar Bunkure ɗin nan
Mai yin nazari don miƙa saƙonni gun al'ummar nan
Shi ke ta du'a'i Rabbi sa gwauraye har tuzurai su san ƙauna
✍🏻
Abul-Mustapha Al-athary
24/6/1444h 🔄 17/1/2023m
Comments
Post a Comment